Ibtila Ambaliya Ruwa Ta Kashe Mutum 32 A Nijar

Kamfanin dillancin labaran Nijar ANP ya ce ambaliyar ruwa ta kashe mutum 32 cikin watannin baya-bayan nan.

Alfijir Labarai ta rawaito Yankin Tahoua da ke kudancin ƙasar ne matsalar ta fi ƙamari, inda mutum 12 suka mutu, sai Maradi mai mutum 10 da Zindir inda mutane shida suka mutu”, kamar yadda ANP ya ruwaito daga ma’aikatar cikin gida ta ƙasar.

Sai Tileberi mai mutum biyu, da kuma Yamai da Diffa masu mutum ɗaiɗai.

Rahoton ya ce mutum tara daga ciki sun mutu ne, bayan da gidajen da suke ciki suka rufta, yayin da 23 suka mutu sakamakon nutsewa a cikin ruwan.

Ruwan sama kamar da bakin ƙwarya da ake samu cikin takiyar kowace damina, na haifar da ɓarna mai yawa a ƙasar.

BBC

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook.   Alfijir Labarai
YouTube.     Best Seller Channel
Twitter.        @Musabestseller
Instagram.  @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai  👇

https://chat.whatsapp.com/Jmw5CBsPV6H3DbSgnlFUHM

Slide Up
x

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *