Aƙalla mutane 50 ne suka mutu yayin da aka yi garkuwa da mata da yara da dama a wani hari da aka kai wani ƙauye a Jihar Zamfara a Nijeriya.
Harin, wanda ‘yan ta’adda da ake kira ‘yan bindiga a yankin suka kai, ya fara ne a daren Alhamis kuma ya ci gaba har zuwa safiyar Juma’a.
Maharan da suka iso a kan babura sun banka wa gine-gine wuta tare da harbin mazauna ƙauyen Tungan Dutse da suka yi ƙoƙarin tserewa, kamar yadda Hamisu Faru, ɗan majalisar jiha, ya tabbatar wa kamfanin dillancin labarai na Anadolu a ranar Asabar.
“Tun daga daren Alhamis har zuwa safiyar yau babu wanda ya samu barci. Wasu mutane sun rasa ‘yan uwa uku daga cikin iyalansu,” in ji Faru ga Anadolu.
An shirya gawawwakin waɗanda suka mutu domin jana’izar gama-gari, inda aka lulluɓe su da farin likkafani a ranar Asabar. Har yanzu ba a tantance adadin mutanen da aka yi garkuwa da su ba, yayin da jami’an yankin ke ci gaba da ƙididdige waɗanda suka ɓace.
TRT Hausa
Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835
Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇
https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t