Daga Aminu Bala Madobi
Jagororin juyin mulki a Jamhuriyar Nijar sun nada sabbin ministoci a sabuwar gwamnati.
Alfijir Labarai ta rawaito cikin wata doka da aka karanta a gidan talabijin na kasar a ranar Alhamis, ta tabbatar da wannan ci gaban.
Firayim Minista Ali Mahaman Lamine Zeine ne zai jagoranci gwamnati mai mambobi 21, tare da janar-janar sabuwar majalisar mulkin sojan da ke jagorantar ma’aikatun tsaro da na cikin gida.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da shugabannin kasashen yammacin Afirka za su gana a yau Alhamis domin yin tir da matakin soji kan gwamnatin mulkin soji, karkashin jagorancin tsohon kwamandan tsaron shugaban kasar, Janar Abdourahmane Tchiani.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
Facebook. Alfijir Labarai
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇
https://chat.whatsapp.com/BW0j8s7exuQ7ojpyCVMtfI