Babbar Kotun jihar Kano mai lamba 1 da ke Sakatariyar Audu Bako, Karkashin mai shari’a babbar alakaliyar jahar Kano Dije Abdu Aboki, ta yanke wa wani magidanci Ado Idris, hukuncin daurin shekaru 19, sakamakon samunsa da yiwa wata karamar yarinya fyade a unguwar Fagge.
Alfijir labarai ta rawaito Barista Fatima Ado Ahmad mai gabatar da kara kuma lauyar gwamnati ta gabatarwa da Kotun shaidu biyar, shi kuma wanda ake tuhuma ya kare kansa.
Mai shari’a ta yi dogon nazari da bin diddigi aka lamarin, inda ta yanke wa wanda aka tuhuma Ado Idris hukuncin daurin shekaru 19 a gidan gyaran hali
Wanda ake zargin dai kotun ta kama shi da laifin lalata da wata yarinya a mabanbantan lokuta.
Gani ga wane dai ya isa wane tsoron Allah
Domin samun sauran shirye shiryenmu zaku iya biyo mu ta wannan shafukan👇
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj