Kotu Ta Hana Gwamnatin Kano, Ƴan Sanda Da DSS Kama Tsohon Gwamna Ganduje

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kano ta hana gwamnatin jihar Kano da jami’anta da ƴan sanda da DSS dai sauran hukumomin tsaro daga kama tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Ganduje da duk wasu makimusantan sa.

Alfijir Labarai ta rawaito Alkalin kotun, Mai shari’a A. M. Liman, a cikin takardar umarnin, mai dauke da kwanan wata 6 ga Yuli 2023 ya amsa wa masu shigar da korafin bukatar su.

“Wadanda ake kara ko su da kansu, ko kuma ta hanyar jami’ansu,jami’ansu, jami’an tsaron su, masu zaman kansu ko wani mutum ko gungun mutane kar su musgunawa, tsoratarwa, gayyata, barazanar kamawa, ko tsare wanda ya shigar da korafi, ko ‘ya’ya ko wani daga cikin danginsa, ko duk wanda aka nada wanda ya yi aiki a karkashin kulawar mai korafi ko kuma ya karbe kadarorin mai korafi da karfi ko ‘ya’yansa ko wani daga cikin danginsa, ko duk wanda aka nada wanda ya yi aiki a karkashin gwamnatin mai korafi har sai an yanke hukunci a kan neman hanawar”. A cewar umarnin kotun

Kotun tace umarnin wucin gadi zai yi aiki har zuwa lokacin da za a saurari ƙorafin da aka shigar a kan tauye ƴancin ɗan adam zuwa ranar 14 ga Yuli, 2023.

Wadanda aka baiwa umarnin za a ba su kundin umarnin sa’o’i 36 daga yau,” in ji alkalin.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook.   Alfijir Labarai
YouTube.     Best Seller Channel
Twitter.        @Musabestseller
Instagram.  @musa_bestseller

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai  👇

https://chat.whatsapp.com/GdLiqZyHuSz5NhjdGoGRGZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *