Labari Mai Dadi: Jami’ar Tazkiyah Dake Zaria Ta Dauki Nauyin Karatun Wasu Tarin Marayu

IMG 203627 02126 1767382599690

Shugaban Jami’ar Mata Zalla Tazkiyah, da ke Zaria Farfesa Ibrahim Ahmad Makari ya ba wa mata marayu gurbin karatu a Jami’ar.

Jami’ar Tazkiyah Zaria ita ce ta farko a Nijeriya wadda mata ne kawai za su yi karatu a cikinta. An zabo wadanda suka cancanta daga sassa daban-daban na Nijeriya.

An bayar da wannan gurbin karatun ne ba tare da la’akari da kabila ko addinin wadda ya samu ba.

Farfesa Ibrahim Garba Satatima, tsohon Shugaban Tsangayar Fasaha da Addinin Musulunci na Jami’ar Bayero, Kano ya yaba wa wannan hidima ga al’umma inda ya kwatanta ta da irin wadda marigayi Gani Fawehinmi ya ba wa matasan Nijeriya a matsayin abin yabawa.

Malamin ya kuma addu’ar fatar samun nasara ga wannan Jami’ar .

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *