Ma’aikatan Kula Da Zirga-Zirgar Jiragen Sama Sun Hana Tashin Jirage A Kano

Alfijr ta rawaito yanayin tashi da saukar jirage ya samu tasgaro a filin jirgin sama na Mallam Aminu Kano, sakamakon zanga-zanga da ma’aikatan hukamar da ke kula da zirga-zirgar jirgin sama ta kasa ke yi.

Alfijr Labarai

Rahotanni sun tabbatar da cewa Jiragen da za su tashi yau Litinin ba su samu damar tashi ba sakamakon rikicikin da Jami an ke yi.

Hakan ta haramtawa Jiragen AZMAN da Max Air tashi, Yadda aka tsara tashin su zuwa Abuja da Lagos, da safiyar litinin

Sakamakon wannan rashin tashin jiragen lamarin ya rutsa da manyan mutane da dama, kama manyan yan siyasa da masu madafun iko hada da attajirai

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *