Hukumar Kula da Fannin Shari’a ta Ƙasa, NJC ta amince da ƙarin girma zuwa alkalancin kotun koli ga Moore Aseimo A. Adumein, alkalin da ya yanke hukuncin zaɓen gwamnan Kano mai cike da rudani.
Alfijir labarai ta rawaito wata sanarwa da Daraktan Yaɗa Labarai na NJC, Soji Oye, an amince da ƙarin girma ga Adumein, duk da kuskure da aka tafka a shari’ar, wanda bayan ya yanke cewa kotun ta tabbatar da hukuncin tirabunal, wanda ya tabbatar da nasar Nasiru Gawuna, sai kuma da kundin hukuncin ya fito, sai aka ga ashe asali korar hukuncin tirabunal din kotun ta yi.
Oye ya ce za a rantsar da alkalami da aka yi wa ƙarin girma bayan shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da majalisar Dattawa sun amice.
Ya ce sauran shugabannin kotuna da aka yi wa ƙarin girma, za a rantsar da su ne bayan gwamnonin jihar da majalisar jihar su sun tantance da amincewa da su.
Daily Nigerian
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/H47OrRBUPHYEeNqV0vwlQp