Ofishin jakadancin Amurka ya gargadi ‘yan ƙasarta kan yiwuwar zanga-zanga a Abuja

FB IMG 1772645925483

Ofishin Jakadancin ƙasar Amurka a Abuja ya yi gargadi ga ‘yan ƙasar Amurka da ke Najeriya kan yiwuwar ɓarkewar zanga-zanga a Abuja, sakamakon ƙarin tashin hankalin da ke tattare da rikicin Amurka/Isra’ila da Iran a gabas ta tsakiya.

A cikin sanarwar da ya wallafa a dandalin X, ofishin ya ce akwai yiwuwar zanga-zanga mai ƙarfi a babban birnin ƙasar, tare da shawartar ‘yan Amurka da su zauna a gidajensu a ranar Laraba, 4 ga Maris.

Sanarwar ta kuma buƙaci su guji wuraren taron jama’a, su riƙa lura da muhallinsu, tare da bibiyar kafafen yaɗa labarai domin samun sabbin bayanai.

Duk da gargaɗin, ofishin jakadancin ya tabbatar da cewa sashen ba da biza da kula da al’amuran ‘yan ƙasa a Abuja da Legas na ci gaba da aiki kamar yadda aka saba.

Daily Nigerian

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *