Rundunar Yan Sanda Sun Kama Mutume 307 A Wani Samame Maboyar Bara Gari A Abuja

FB IMG 1707747699386

Rundunar yan sanda a Abuja, babban birnin Nijeriya ta ce ta kai samame wata matattarar miyagu inda ta kama mutum dari uku da bakwai da ake zargi da aikata laifuka.

Alfijir labarai ta rawaito Kwamishinan yan sanda a Abuja, CP Benneth C. Igwe ne ya jagoranci tawagar rundunar ‘Operation Velvet’ wajen kai samame kan matattarar da ke Gidan Dambe a yankin Dei-Dei zuwa Zuba.

Yayin binciken, an gano bindiga daya da alburusai goma sha biyar a hannun wani da yake ikirarin shi jami’in hukumar tsaro ta farin kaya ne.

A cewar sanarwar da kakakin rundunar, SP Josephine Adeh ta wallafa a shafin X, sauran kayayyakin da aka gano sun hada da babura da kunshin tabar wiwi da haramtattun kwayoyi da ake zargi mutanen sun sace ne daga hannun mutanen da ba su ji ba su gani ba.

Kwamishinan yan sandan ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan mutanen da aka kama.

A makon da ya gabata ne aka kaddamar da rundunar ta musamman domin kawo karshen duk wasu miyagun laifuka a Abujar.

Kwamishinan ya kuma gargadi yan sanda kan tatsar jama’ar sannan su nuna kwarewa wajen aiwatar da ayyukansu.

FB IMG 1707747706469
📸 Nigerian Police
FB IMG 1707747704115
📸 Nigerian Police

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H3iC9eVfJI012LJzvCQn5V

Slide Up
x

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *