Sakon Shugaban Nijeriya Tinubu Ga Gwamnoni Kasar

FB IMG 1710509750089

Ku Ajiye Bambancin Siyasa ku Fuskanci Al’ummarku

Alfijir labarai ta rawaito shugaban kasa Bola Tinubu ya yi kira ga gwamnonin jihohi da su ajiye bambancin siyasa a gefe su hada kai da gwamnatin tarayya wajen gina kasa.

Tinubu ya yi wannan kiran ne a lokacin bude-bakin azumin watan Ramadan tare da gwamnoni a fadar gwamnati da ke Abuja, a jiya Alhamis.

Ya kuma jaddada muhimmancin ajiye siyasa a fuskanci mulki, inda ya ce akwai bukatar hadin kai a tsakanin masu ruwa da tsaki.

“Tunda mun fahimci bukatar gina al’ummarmu tare, lokacin siyasa ya wuce. Yanzu lokaci yayi na mulki.

“Mu ‘yan uwa daya ne kuma iyayenmu daya; mu na zaune a gida daya, amma a dakuna daban-daban mu ke kwanciya. Dole ne mu hada kai da yada soyayya a tsakanin juna,” inji shi

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/CJ2q8cmhhOxFY6OEgwV5vk

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *