Shugaba Tinubu ya amince da karawa Buba Marwa wa’adin shugabancin NDLEA

FB IMG 1763115335811

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da sake nada Birgediya-Janar Mohammed Buba Marwa (mai ritaya) a matsayin Shugaban Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA) na wani sabon wa’adi na shekaru biyar.

Marwa, wanda tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada a watan Janairu 2021, zai ci gaba da jagorantar hukumar har zuwa shekara ta 2031. Kafın wannan, ya jagoranci Kwamitin Shugaban Kasa kan Kawar da Shan Miyagun Kwayoyi daga 2018 zuwa 2020.

Tsohon hafsan soja ne dan asalin jihar Adamawa, kuma ya taba zama gwamnan soji na jihohin Legas da Borno. Marwa ya yi karatu a Makarantar Soja ta Najeriya da kuma Kwalejin Tsaro ta Najeriya (NDA).

Sanarwar ta fito ne daga Bayo Onanuga, Mai Bai wa Shugaban Kasa Shawara kan yada labarai.

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *