Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bada umarnin a cire sunan Maryam Sanda — wadda aka yanke wa hukuncin kisa a shekara ta 2020 bisa laifin kashe mijinta, Bilyaminu Bello — daga cikin jerin waɗanda aka tanadi musu afuwar shugaban ƙasa.
Rahotanni sun nuna cewa Sanda na cikin jerin mutanen da ake tunanin za su samu rangwame, sai dai an soke sunanta bayan umarnin shugaban ƙasa da ya haramta bayar da afuwa ga waɗanda aka tabbatar da laifuka masu tsanani.
A cewar sabon umarnin, duk wanda aka samu da laifin garkuwa da mutane, safarar miyagun ƙwayoyi, safarar mutane, zamba, da kuma mallaka ko safarar makamai ba bisa ka’ida ba, ba za su sake cin gajiyar afuwar shugaban ƙasa ba.
Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835
Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇
https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t