Ta’addaci! An Tsinci Gawar Ɗan Jarida A Abuja

FB IMG 1717108061650

Rahotanni sun bayyana cewa an tsinci gawar wani dan jarida na kamfanin sadarwa na Atar Communication, mamallakan gidan talabijin na Liberty TV/Radio a ranar Laraba a Abuja, kwanaki biyar bayan an bayyana bacewarsa.

Alfijir labarai ta ruwaito Ɗan jaridar, mai suna Joel Waksi, an ce ya bar ofis da misalin karfe 9 na daren ranar Juma’a kuma ana sa ran zai dawo bakin aiki da karfe 2 na rana a ofishin su da ke Mpape.

Babban Manajan Kamfanin, Balarabe Muhammad, yayin da yake tabbatar da faruwar lamarin ga City & Crime, ya ce rundunar ‘yan sandan reshen Mpape ta sanar da cewa an ga gawarsa kusa da yankin Panteka kuma an ajiye gawar a babban asibitin Kubwa

Ya ce an caka masa wuka a wuyansa, kuma wayarsa ta bata.

Ya ce, “An yi zargin cewa masu ƙwacen waya ne suka kai masa hari,” ya kara da cewa watanni biyu baya, ya tsallake rijiya da baya, inda aka caka masa wuka a karkashin cikinsa, amma aka yi masa magani ya warke,” in ji shi.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *