Tinubu ya amince da shekaru 65 na ritaya ga likitoci da ma’aikatan lafiya

FB IMG 1738763286178

Daga Aminu Bala Madobi

Shugaba Bola Tinubu ya amince da shekarun ritaya ga likitoci da sauran ma’aikatan kiwon lafiya daga shekaru 60 zuwa 65.

Dakta Mannir Bature, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Likitocin Najeriya, NMA, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a yau Laraba a Legas.

Bature ya ce an umurci ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Muhammad Pate da ya gabatar da amincewar shekarun ritayar a hukumance.

Ya ce Pate ne ya gabatar da wannan sauyin manufofin a lokacin wani babban taro da shugaban NMA, Farfesa Bala Audu, da masu ruwa da tsaki a fannin lafiya.

Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news zaku iya bibiyarmu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/IqPyC2oGzdQ9NudcMXFqHZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *