Tsalle Ɗaya! An kama jarkokin manja maƙare da alburusai a Abuja

FB IMG 1742875672522

Mutumin da aka kama ya ce an biya shi N100,000 domin karɓo alburusan daga wajen wani mutum a Jihar Nasarawa.

Rundunar ‘yan sandan Birnin Tarayya ta ce ta kama damin alburusai 488 da aka ɓoye a jarkar manja a tashar mota.

Mataimakin kwamishinan ‘yan sandan da ke kula da sintiri na musamman a Abuja, DCP Ishaku Sharu, ne ya bayyana hakan lokacin da yake holen wanda ake zargin a ofishin rundunar a ranar Litinin.

Ya ce rundunar ta samu nasarar kama wanda ake zargin ne bisa tallafin wasu jami’an ƙungiyar masu sufurin motocin haya (NURTW).

Kazalika, ya ce sun kama wanda ake zargin ne ɗan asalin Jihar Katsina, ɗauke da harsashi 488 na bindigogin AK-47 da ya ɓoye a jarkokin manja.

DCP ya ce bayan rutsa shi ne ya bayyana musu cewa wani Yakubu Kacalla ne ɗan garin Funtua da ke Katsinan ya biya shi N100,000 domin karɓo masa kayan daga wajen wani mutum a Jihar Nasarawa.

Yanzu haka dai wanda ake zargin na hannun ‘yan sanda inda suke ci gaba da bincike domin kamo sauran masu hannu a safarar makaman.

Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news ku shiga nan  👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/KoLt2IMlnQfJPP6zNrcNKD

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *