Yadda a kwanaki 100, VON ta farfaɗo, ci gaba ya bayyana da kuma fatan fin haka nan gaba — Daga Jibrin Baba Ndace

IMG 20240131 WA0052

A zafin ranar 29 ga watan Oktoba, 2023 ne aka samu wani canji na alheri da ya lulluɓe harabar Voice of Nigeria (VON) mai cike da sa’ida, sakamakon naɗin da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya yi mini a matsayin Darakta-Janar na gidan rediyon na ƙasa, inda hakan ya zamto wani ɗamba na sauyin zamani a kafar yaɗa labaran ta ƙasa.

Bikin karɓar aiki daga hannun wanda na gada, Osita Okechukwu ya wuce a ce biki ne na sallamar ma’aikaci. Da ga karɓar shugabancin, guguwar sauyi ta fara kaɗa wa bayan na halarci taron AFRICAST 2023 a Legas. Sai na yi amfani da wannan damar na ziyarci cibiyoyin watsa shirye-shiryen tashar ta mu da ke Ikoyi da Ikorodu, inda hakan ya bani kwarin gwiwar cewa akwai dama mai ƙarfi da zan samu na kawo gagarumin ci gaba a gidan rediyon.

Dawowa ta shelkwatar VON da ke Abuja kuma, sai na fuskanci akwai aiki ja a gaba na. A yanayin lalacewar gine-gine da kayan aiki da na gani a cibiyar mu ta Ikko, sai na ji cewa ya zama wajibi na tashi tsaye na kawo gyara cikin gaggawa.

Duk da cewa kusan hakan yanayin ya ke a cibiyar watsa shirye-shiryen mu ta Lugbe a Abuja, akwai abinda ya bani ƙarfin gwiwa, shi ne wutar sola da na tarar. Sai na fahimci cewa wato akwai ɗumbin nasarori a VON, amma ana buƙatar jajirtaccen shugaba da zai farfaɗo da ita.

Bayan gine-gine da kayan aiki, ma’aikata su ne ƙashin bayan VON, sai dai kuma kash! akwai ƙarancin karsashi a tare da su ma’aikatan gidan rediyon a duka tashoshin namu na Abuja da Legas sakamakon rashin biyan su alawus-alawus na su da kuma kuɗaɗensu na ƙarin matsayi. Wannan ƙalubale ne da ya ke buƙatar kawo ɗauki cikin gaggawa domin samun gaba mai kyau.

Tun asali, kamata ya yi a samu wani kundi na tsare-tsare. Zaburar da ma’aikata na buƙatar ƙirƙiro da dabarun inganta walwalar su da kuma ƙara musu matsayi akai-akai lokacin da ya dace da kuma basu lambobin yabo bisa ƙwazon su a aiki. Kada kuma a manta da cewa haɗin kai tsakanin shugabanni da ma’aikata shi ne babban sinadarin kawo sauyi Na ci gaba a ma’aikata.

Halastar mu zuwa babban taron UNESCO na duniya, karo na 42 da aka yi a birnin Paris da kuma taron ranar rediyo na duniya a Dubai, ba wai mun je yawon buɗe-ido ba ne, sai dai wata babbar dama ce ta samun damammaki daga ƙasashen duniya. Waɗannan tarukan wata babbar dama ce ta nuna wa duniya irin ƙwazon VON na watsa shirye-shirye daidai da yadda ya ke a duniya da kuma ƙulla alaƙa, duk a ƙoƙarin ta na zama a aji ɗaya da manyan kafafen yaɗa labarai na duniya.

Ganawar farko ta shugabannin VON da ta gudana a ranar 19 ga watan Disamba, 2023, ba wai an yi zaman hira ne kawai ba, sai dai zaman ya kasance wata ɗamba ce aka kafa wajen samar da haɗin gwiwa domin fitar da dabarun aiki da za su ƙara taimaka wa gidan rediyon ya cimma muradun sa.

Aiyuka na bi-da-bi me ya haifar da nasarar da mu ka samu ta ganawa da kwamitin majalisar dattawa kan yaɗa labarai da wayar da kan al’umma, kare kasafin kudin da mu ka yi wa kwamitocin majalisar dattawa da na majalisar wakilai da kuma ziyarar aiki da mu ka kaiwa Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da kan Al’umma, Alhaji Mohammed Idris. Waɗannan aiyukan sun kasance tubalin mu na gina alaƙa, wacce za ta samar mana da taimako da kuma fahimtar juna.

Hakazalika, alaƙar da mu ka ƙulla da ma’aikatun gwamnati da masu zaman kansu, da suka hada da Thunderbird, Image Marchants Promotions Limited, SEMEDAN, GOTNI, NIPR, Ciyaman na NUJ a Minna da kuma wakilci da ga Dangote Group da Jaiz Bank, ba wai ziyara ba ce kaɗai, sai dai sun zamto tattaunawa da za su buɗe kofa, su gina mana gadoji da kuma alaƙa da za su taimaka wa VON ta kai gaci.

Sannan, ziyarorin da muka kai wa Media Trust, National Orientation Agency, News Agency of Nigeria, Nigerian Diaspora Commission da NTA da kuma manyan shugabannin sojoji ya nuna ƙwazon mu na kawo gyara mai inganci a VON tare da bata suffar da ta ke buƙata.

A kwanaki 100 na farko a matsayin Darakta-Janar, na bada umarnin cewa duk wani ɗan hidimar ƙasa (NYSC) da masu koyon aiki a VON, dole a basu horo na musamman, da nufin su ji a ransu kamar su ma ma’aikata ne a tsawon lokacin da za su yi a gidan rediyon. Daɗin daɗawa kuma mun ƙulla alaƙa da Guards Polo Club da ƙungiyar shugabannin ma’aikatu ta Afirka domin jawo hankalin al’umma ga irin aikace-aikacen VON.

Bayan duk wadannan, irin bayanan sam-barka da ke fitowa daga bakunan ma’aikatan VON masu albarka, ya ƙara mana ƙaimi da ƙwarin gwiwa. Maida hankali da mu ka yi wajen gyara lalatattun kayan aikin mu da neman tallafin gwamnati wajen farfaɗo da tashar mu ta Lugbe ya nuna yadda shugabancin mu ke da zuciyar kawo gyara da kuma ɗaukaka VON.

A yayin da muka cika kwanaki 100 da karɓar ragamar shugabancin VON, magana a ke yi ta fara ganin guguwar sauyi ta fara kaɗa wa. Kalubalen da mu ka taras ya zamto wani ginshiƙi na gyara mai inganci. Sannan, dabarun da mu ke ɓullo da su sau ɗau saiti na fito dartabar VON ba wai a matsayin shahararren gidan rediyo ba, har ma ta zamto a bar koyi a fannin watsa shirye-shirye a faɗin duniya. Yayin da ake ci gaba da samar da hanyoyin gyara, lokaci kaɗai mu ke jira da zai fito da VON da har karan ta zai kai tsaiko a idon duniya.

Mallam Jibrin Ndace shi ne Darakta-Janar na VOICE of Nigeria, VON. Tashar watsa labarai na duk duniya ta Nijeriya.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H3iC9eVfJI012LJzvCQn5V

Slide Up
x

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *