Yadda Lauya Abba Hikima Fagge Ya Magantu Kan Bawa Dan Kwankwaso Kwamishina A Kano

FB IMG 1711598093345 edit 22401135259601

Lauya Abba Hikima Fagge ya dan gwagwarmayar tsage gaskiya komai sa cinta ya magantu kan mikamin da gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya tura sunan Mustapha Kwankwaso Kwamishina a Kano.

Duk da kusancin da lauyan ke da shi tsakanin sa da wannan gwamnatin amma bata hanashi idan yaga abinda yake ganin a fahimtarsa ba dai dai bane ba yayi magana.

Naɗa yaron Kwankwaso a irin wannan lokaci kuskure ne, ba komi bane ya halatta zai zama ya Kamata.

Irin wannan halayen sune aka dinga zargin gwamnatin da ta shuɗe da jawo makusanta da ƴaƴa cikin harkar jagoranci, yin hakan ba daidai bane.

Shi a harkar jagoranci chanchanta ake dubawa ba kusanci ba, dan haka yin irin wannan naɗin kuskure ne.

Nada Mustapha a matsayin kwamishina shi ake kira kusanci ba chanchanta ba a tsarin Demokradiyya. Inji Barista Abba Hikima.

Barista Abba hikima ba wannan bane karon farko da yake tsage gaskiya ya faɗeta komin da cinta a jihar.

Ga Abba Hikima da bakinsa a Tattaunawarsu da Arewa Radio
👇👇

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/CJ2q8cmhhOxFY6OEgwV5vk

Slide Up
x

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *