‘Yan bindiga Sun Kai Wani Mummunan Hari Gidan Yari Kuje Da Ke Birnin Tarayya Abuja


Alfijr
Alfijr ta rawaito a daren Talata ne wasu ‘yan bindiga suka kai hari a Cibiyar gyaran hali da tarbiyya ta Kuje da ke Abuja, babban birnin kasar da bama-bamai.

Harin ya zo ne a wani mataki da ake ganin sun dauka na shiga ginin tare da ‘yanto wasu daga cikin mambobinta.

Alfijr

An kai hari gidan yarin da misalin karfe 10:27 na dare. tare da bama-bamai da harbin bindiga.

Bincike ya nuna cewa ’yan bindigar da ake zargin sun kai hari ne a bayan harabar.

Fashewar da karar harbe-harbe ya jefa yankin cikin rudani da firgici yayin da mazauna yankin suka yi ta tururuwa domin tsira da rayukansu.

A halin da ake ciki dai har yanzu mahukunta ba su mayar da martani kan lamarin ba

Alfijr

Karin Bayani na nan tafe

Slide Up
x