Za mu Gudanar Da Gagarumar Zanga-zanga Idan Ba a Soke Harajin Tsaron Intanet Ba  — In Ji Ƙungiyar Kwadago

FB IMG 1715255487941

Ƙungiyar ƙwadago ta TUC a Najeriya ta yi barazanar gudanar da gagarumar zanga-zanga tare da dakatar da al’umura a faɗin ƙasar matuƙar gwamnatin tarayya ba ta soke sabon harajin tsaron intanet da Babban bankin ƙasar ya ɓullo da shi ba.

Alfijir labarai ta rawaito kungiyar ta yi barazanar ce a wata sanarwa da ta fitar yau Laraba, wadda ta samu sa hannun shugaban ƙungiyar, Festus Osifo.

Hakan na zuwa ne bayan ita ma ƙungiyar ƙwadago ta TUC ta soki lamirin sabon harajin, wanda ta bayyana a matsayin wani gagarumin nauyi da gwamnati ke ɗora wa talaka.

A ranar Talata ne Babban Bankin Najeriya ya fitar da wata sanarwa wadda ke neman a cire harajin kashi 0.5 cikin ɗari kan duk wata hada-hadar tura kuɗi da mutanen ƙasar suka yi ta intanet.

Sanarwar TUC ta ci gaba da cewa “babu dabara wajen fito da irin wannan haraji daidai lokacin da ƴan Najeriya ke fama da tsadar rayuwa sanadiyyar faɗuwar darajar naira da ƙarin farashin man fetur da na lantarki.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/IUuk7jeH4yvAkwOmbOCSfl

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *