Zanga-zanga Ta Barke a Jos Sakamakon Kashe-kashe Na Harin ‘Yan Bindiga

FB IMG 1745253519234

Daga Aminu Bala Madobi

Wasu mazauna garin Jos, babban birnin jihar Filato, sun gudanar da zanga-zangar nuna adawa da sace-sacen mutane da kashe-kashe da ‘yan bindiga ke yi a jihar.

Ayarin mutanen karkashin jagorancin shuwagabannin kiristoci da suka hada da shugaban kungiyar kiristoci ta jihar, Rev. Polycarp Lubo, ta faro ne a safiyar yau litinin, wanda ya haifar da cunkoson ababen hawa.

Zanga-zangar ta baya-bayan nan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da samun munanan hare-hare da ‘yan bindiga ke kai wa a al’ummomi daban-daban, inda aka kashe sama da mutane 100 a karamar hukumar Bokkos da Bassa cikin makonni biyu da suka gabata.

A halin yanzu dai ana ci gaba da gudanar da jerin gwano na yaki da hare-hare da kashe-kashen da wasu ‘yan bindiga suka yi wa al’umma a kauyuka da yankunan jihar Filato a Jos babban birnin jihar, bisa jagorancin kungiyar Kiristoci.

Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news ku shiga nan  👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/KoLt2IMlnQfJPP6zNrcNKD

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *