Shugaban Najeriya Bola Tinubu zai kai ziyarar aiki jihar Adamawa a ranar Litinin

FB IMG 1766052696951

Shugaban kasa, Bola Tinubu, zai kai ziyara ta aiki jihar Adamawa ranar Litinin, kasa da sa’o’i 48 bayan irin wannan ziyara da ya kai a jihar Kebbi.

Sanarwar ta fito ne daga hannun Mai Ba Shugaban Kasa Shawara kan Harkokin Yada Labarai da Dabaru, Bayo Onanuga, ranar 15 ga Fabrairu, 2026.

A yayin ziyarar ta yini guda, Shugaba Tinubu zai kaddamar da wasu manyan ayyuka da aka kammala, sannan ya gana da manyan jami’an gwamnati da sarakunan gargajiya na jihar.

Daga cikin ayyukan da za a kaddamar a babban birnin jihar, Yola, da Jimeta, akwai titin Galadima Aminu mai layuka takwas da ke hada Gimba da babban birnin jihar.

Sauran ayyukan sun hada da sabon dakin taro na zamani, gyaran kotun koli ta jihar, sabon ginin ofisoshin gwamnati, da kuma sabunta Gidan Gwamnati.

DCL

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *