Gwamnatin Najeriya Ta Ayyana Ranakun Hutun sallah ƙarama

FB IMG 1742320893164

Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin, 31 ga Maris, da Talata, 1 ga Afrilu, a matsayin ranakun hutu domin bukukuwan Sallah Ƙarama

Ministan Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da Magdalene Ajani, Babbar Sakatariyar Ma’aikatar, ta fitar a ranar Laraba.

Ministan ya taya daukacin al’ummar Musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan cikin nasara, tare da yin kira ga al’ummar 3su rungumi dabi’un hakuri, tausayi, kyauta, da zaman lafiya.

Ya kuma bukaci ‘yan Najeriya su yi amfani da wannan dama wajen yin addu’o’i don zaman lafiya, daidaito, da ci gaban kasa.

Tunji-Ojo ya yi fatan cewa wannan biki na Sallah Ƙarama zai kara hadin kai da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai da kabilu daban-daban a kasar.

A karshe, ya bukaci jama’a da su yi bukukuwa cikin lumana da kiyaye doka, tare da tunawa da marasa galihu ta hanyar ayyukan alheri .

Gwamnati ta kuma aika da fatan alheri na Eid Mubarak ga daukacin al’ummar Musulmi, tana mai addu’ar Allah Ya kawo albarka, nasara.

For more information about  Alfijir labarai/Alfijir news follow here  👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/KoLt2IMlnQfJPP6zNrcNKD

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *