An yi Garkuwa Da Wani D P O A Nigeria

 

 Wani Labari daga jihar Edo a Najeriya na cewa an yi garkuwa da wani DPO a jihar.

BBC ta ruwaito cewa an sace ɗan sandan mai suna CSP Ibrahim Aliyu Ishaq wanda shi ne DPO na ofishin yan sanda da ke Fugar, a kan hanyar Auchi zuwa Agenebode a jihar Edo.

 CSP Ishaq kafin komawarsa jihar Edo yayi aiki a ofishin ƴan sanda da ke Dakata a jihar Kano.

Rahotanni sun tabbatar da Cewar a bana dai an kai hare-hare ga ofisoshin yan sandan Najeriya da dama musamman a kudancin Najeriya inda aka ƙona Chaji office a ƙwace makamansu.

Allah ya dawwamar mana da zaman lafiya a wannan kasar tamu baki daya ameen. 

Slide Up
x