Badakala! EFCC ta kama masu makarantar koyar da damfara

FB IMG 1737210473377

Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta kasa EFCC ta bankado wani waje da ake kyautata zaton cewa ana koyar da damfara a birnin Benin na jihar Edo.

EFCC ce ta sanar da hakan cikin wata sanarwa data fitar a shafin ta na X a ranar alhamis data gabata, sannan tace an kama mutane 25, masu damfarar mutane a wajen.

Sanarwar tace, EFCC ta samu nasarar kama mutanen a harin da takai bayan samun bayanan sirri akan cewa ana yin amfani da wani gini don koyawa matasa damfarar Yahoo, da saurin nau’in cutar mutane a kafar internet.

Cikin abubuwan da EFCC ta kama a gurin koyar da damfarar sun hadar da motoci guda 6, da na’ura mai kwakwalwa wato (Computer).

Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news zaku iya bibbiyarmu ta 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *