Baya Ta Haihu! Maganar Rage Kudin Fom Da Farfesa Ya Ce Yayi Shifcin Gizo Ne – Barr Hassan T Kyaure

Farfesa Da Barasta

Bayan sanarwar da shugaban hukumar zabe ta jihar Kano Farfesa Malumfashi yayi na rage kudin fom din takarar zaben kananan hukumomi baya ta haihu.

Alfijir Labarai ta rawaito Barasta Hassan Tanko Kyaure ya ce maganar rage kudin Fom da Farfesa Malumfashi yayi shifcin Gizo ne babu alamar kamshin gaskiya cikinsa.

Kyaure ya kara da cewar maganar da Farfesa yayi ta cewar sun rage kudin fom bisa umarnin da kotu ta bayar na karar da jam’iyyu guda uku suka shigar, wannan abu ya bamu mamaki a matsayinsa na Farfesa mai daraja.

“Don haka nake kira ga Jama’a da su yi watsi da wannan maganar tasa, domin babu kamshin gaskiya cikinta.”

Barasta ya kara da cewar, odar da kotu ta bayar a gaban mai shari’a  Emeka Unweke na babbar kotun tarayya, cewa tayi, ta dakatar da hukumar zabe ta jihar Kano karbar Naira miliyan 10 daga dan takarar ciyaman, su kuma kansiloli miliyan 5, har sai ta gama sauraron shariar, zuwa 25th ga watan Satumba din nan 2024.

Don haka muke jan kunnen jam’iyyu kar wanda ya yarda da wannan zancen har ya bashi kudinsa! Na sha mamaki a matsayi irin na Farfesa ya dinga irin kokarin shirya zance da sunan kotu, domin ya karbi kudaden jama’a.

Screenshot 20240913 155453 CamScanner
Order
Screenshot 20240913 155501 CamScanner
Order
Screenshot 20240913 155508 CamScanner
Order

Domin samun sauran shirye shiryenmu zaku iya biyo mu ta wannan shafukan👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *