Daƙyar ƴan Nijeriya ke cin abinci sau ɗaya a rana, ya kamata shugaban ƙasa ya tashi tsaye — In Ji NLC

Screenshot 20240723 134721 Facebook

Shugabannin kungiyoyin kwadago na kasa, sun shawarci shugaban kasa Bola Tinubu da ya dakile zanga-zangar da ta kunno kai a fadin kasar ta hanyar tattaunawa da wadanda su ke shirya ta.

Daily Trust ta rawaito cewa daruruwan ‘yan Najeriya na gangami domin gudanar da zanga-zanga a fadin kasar .

Da ya ke tsokaci kan lamarin, shugaban kungiyar kwadago ta ƙasa (NLC), Joe Ajaero, ya bukaci shugaban kasar da ya gano jagororin zanga-zangar ya tattaunawa da su.

Ajaero ya kuma yi kira ga Tinubu da ya saurari kukan jama’a, inda ya kara da cewa miliyoyin ‘yan Najeriya ba sa jin dadin halin kuncin da kasar ke ciki.

Shugaban ƙwadagon ya lura da takaicin cewa matsin tattalin arzikin ƙasar ya sanya iyalai da yawa ba sa iya cin abinci sau ɗaya a rana.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *