Shugabannin kungiyoyin kwadago na kasa, sun shawarci shugaban kasa Bola Tinubu da ya dakile zanga-zangar da ta kunno kai a fadin kasar ta hanyar tattaunawa da wadanda su ke shirya ta.
Daily Trust ta rawaito cewa daruruwan ‘yan Najeriya na gangami domin gudanar da zanga-zanga a fadin kasar .
Da ya ke tsokaci kan lamarin, shugaban kungiyar kwadago ta ƙasa (NLC), Joe Ajaero, ya bukaci shugaban kasar da ya gano jagororin zanga-zangar ya tattaunawa da su.
Ajaero ya kuma yi kira ga Tinubu da ya saurari kukan jama’a, inda ya kara da cewa miliyoyin ‘yan Najeriya ba sa jin dadin halin kuncin da kasar ke ciki.
Shugaban ƙwadagon ya lura da takaicin cewa matsin tattalin arzikin ƙasar ya sanya iyalai da yawa ba sa iya cin abinci sau ɗaya a rana.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj