Da ƊUMI DUMINSA: Tinubu ya amince da naɗin Mahmud Yakubu a jakadan Qatar, Fani-Kayode zuwa Jamus, da wasu 63.

FB IMG 1754600090124

Daga Aminu Bala Madobi

Shugaban ƙasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da tura sabbin jakadun Najeriya guda 65 zuwa ƙasashe daban-daban da kuma Zauren Majalisar Ɗinkin Duniya.

A cikin jerin akwai jakadu 31 na ma’aikatan diflomasiyya na dindindin (career ambassadors) da kuma 34 waɗanda ba ma’aikatan diflomasiyya na dindindin ba (non-career ambassadors).

Majalisar Dattawa ta tabbatar da waɗannan jakadu tun a watan Disambar da ya gabata.

Jerin wasu daga cikin jakadun da aka tura (Non-Career Ambassadors)

Sanata Grace Bent – Lome, Togo
Sanata Ita Enang – Afirka ta Kudu
Victor Ikpeazu – Spain
Nkechi Linda Ufochukwu – Tel-Aviv, Isra’ila
Mahmud Yakubu – Qatar
Paul Oga Adikwu – Vatican City
Vice Admiral Ibok-Ete Ekwe Ibas – Philippines
Reno Omokri – Mexico
Abasi Braimah – Hungary
Angela Adebayo – Portugal
Olumilua Oluwayimika Ayotunwa – Japan
Ifeanyi Ugwuanyi – Greece
Chioma Priscilla Ohakim – Poland
Aminu Dalhatu – Birtaniya (United Kingdom)
Abdulrahman Dambazau – China
Tasiu Musa Maigari – Gambia
Olufemi Pedro – Australia
Muhammed Ubandoma Aliyu – Argentina
Lateef Kayode Are – Amurka
Joseph Sola Iji – Rasha
Jimoh Ibrahim – Wakilin dindindin a Majalisar Ɗinkin Duniya
Femi Fani-Kayode – Jamus
Isaak Folorunso Adewole – Canada
Fatima Florence Ajimobi – Austria
Lola Akande – Sweden
Ayodele Oke – Faransa
Yakubu N. Gambo – Saudiyya
Nora Ladi Daduut – Koriya ta Kudu
Joe Okocha – Ireland
Kulu Haruna Abubakar – Tunisia
Jerry Samuel Manwe – Trinidad and Tobago

Jakadu na ma’aikatan diflomasiyya (Career Ambassadors)
Wasu daga cikin waɗanda aka tura sun haɗa da:

Nwabiola Ezenwa Chukwumeka – Côte d’Ivoire
Besto Maimuna Ibrahim – Nijar
Mohammed Mahmud Lele – Algeria
Ahmed Mohammed Monguno – Masar
Jane Adams Michael – Jamaica
Alexandra Clark-Omeru – Zambia
Geoffrey Lioma David – Mali
Yvonne Ehinosen Odumah – Equatorial Guinea
Segun Ige – Lebanon
Ruben Abimbola Samuel – Italy
Ogechukwu Kingsley Onaga – Mozambique
Umar Magaji – DR Congo
Muhammad Saidu Dahiru – India
Abdussalam Habu Zayyad – Senegal
Shehu Ilu Barde – Ghana
Aminu Nasir – Ethiopia
Abubakar Musa – Chadi
Mohammed Idris Haidara – Netherlands
Bako Adamu Umar – Morocco
Olatunji Ahmed Sulu Gambari – Malaysia
Romata Mohammed Omobolanle – Tanzania
John Shamah – Botswana
Hamza Mohammed Salau – Iran
Ibrahim Danlami – Kenya
Adeola Mopelola Ibrahim – Benin
Adebayo Emmanuel Ayeni – Belgium
Wahab Adekola Akande – Switzerland
Esther Arewa – Namibia
Joseph John Gergadi – Gabon
Luther Ayo-Kalata – Sierra Leone
Danladi Yakubu Nyaku – Sudan
Bello Dogon-Daji Haliru – Thailand

Najeriya ta riga ta samu amincewar gwamnatin Birtaniya ga sabon Babban Jakadan Najeriya da aka naɗa, wato Ambasada Aminu Dalhatu. Haka kuma, Faransa ta amince da naɗin Ambasada Ayo Oke.

Ma’aikatar ta kuma tura sunayen sauran jakadun zuwa ƙasashen da za su yi aiki domin neman amincewar su, kamar yadda dokokin diflomasiyya suka tanada.

Shugaba Tinubu ya umarci Ma’aikatar Harkokin Waje da ta gaggauta fara shirin horaswa ga sabbin jakadun kafin su fara aiki a ƙasashen da aka tura su.

Sanarwar ta fito ne daga Mai ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Harkokin Yaɗa Labarai, Bayo Onanuga.

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *