Gwamnan Kano Ya Amince Da Miliyan N93.8 Na Tallafin Karatu Ga Ɗalibai 179 ‘Yan Asalin Jihar Dake Karatu Fannin Shari’a

FB IMG 1764772548155

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da bada jimillar N93.8 miliyan a matsayin tallafin karatu ga dalibai 179 ‘yan asalin Jihar Kano da ke karatu a Nigerian Law School (Makarantar Dokoki).

An ce kowanne ɗalibi daga cikin waɗannan ya samu kudin tallafi don karatunsa, wanda zai taimaka wajen rage musu nauyin kuɗaɗen karatu har a makarantar.

Wannan tallafi ya zo ne a matsayin wani ɓangare na shirin gwamnati na tallafa wa ‘yan asalin jihar wajen samun ilimi mai zurfi a fannin shari’a.

Sakataren Gwamnatin Jihar Kano ne ya wakilci Gwamna Abba Kabir Yusuf wurin gabatar da wannan sanarwa a taron da aka shirya domin bayar da tallafin.

Radio Kano

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *