An kashe mutum akalla 76 a wani hari da aka kai cikin jihar Filato, da ke tsakiyar Najeriya.
Alfijir labarai ta rawaito mai magana da yawun gwamnatin jihar Gyang Bere, shi ya tabbatarwa da BBC faruwar lamarin.
Ya ce gwamnan jihar Caleb Mutfwang ya bayar da umarnin kama waɗanda suka kai harin domin su fuskanci hukunci.
Gwamnan ya kuma shawarci jama’a da kwantar da hankali tare da sanar da hukumomin tsaro dukkan wani abu da ba su gamsu da shi ba.
Kananan hukumomin da hare-haren suka shfa sun haɗa da Bokkos da kuma Barikin Ladi da ke jihar ta Filato.
Sai dai rahotanni na cewa alkalumman waɗanda suka rasa rayukansu na iya karuwa kasancewar hukumomin tsaro da haɗin gwiwar ƴan sa kai da kuma mafarauta da suka bazama a cikin daji, na ci gaba da gano ƙarin wasu gawawwaki.
Wani tsohon ɗan majalisar dokokin jihar Filato Bala Fwanje wanda ya fito daga yankin da lamarin ya faru, ya shaida wa BBC cewa sabon farmakin yana da ban tsoro duba da cewa ba Barikin Ladi ko Bokkos ne kaɗai ke fuskantar barazana ba, inda ya ce har da wasu kauyuka da ke faɗin jihar.
Hukumomi sun ce kawo yanzu ba a san waɗanda suka kai sabon harin ba da kuma musabbabin yin haka.
A baya dai jihar Filato ta fuskanci rikice-rikice masu alaka da kabilanci, da kuma tsakanin manoma da makiyaya.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/H47OrRBUPHYEeNqV0vwlQp