Iyalan marigayi Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Ado Bayero, sun nesanta kansu daga wata dangata da wata mata da ake cewa matar Marigayi Sarki Ado ce a jihar Edo.
Alfijir Labarai ta rawaito wannan na kunshe wata sanarwa da suka fitar a ranar Asabar mai ɗauke da sa hannun Aminu D. Ahmad, tsohon Babban Jami’in Tsaron Sarkin Kano Alhaji Ado Bayero, ta ce labarin ko kaɗan ba gaskiya ba ne, wani shiri ne na ɓata sunan marigayin.
Idan zaku iya tunawa kwanakin baya gwamnan jihar Kano ya sanar da biya wa Zainab Jummai, wacce take ikirarin ‘yar Marigayi Sarkin Kano ce Alhaji Dakta Ado Bayero, kudin haya a gidan da ita da mahaifiyarta ke zaune a Lagos.
Aminiya
Domin samun sauran shirye shiryenmu zaku iya biyo mu ta wannan shafukan👇
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj