Rundunar ‘yan sandan ta tabbatar da cewa an kaiwa jami’anta biyar hari a Wuse. Abin takaici, an tabbatar da mutuwar jami’ai biyu, yayin da wasu uku kuma ba su hayyacinsu a halin yanzu.
Alfijir Labarai ta rawaito rundunar ‘yan sandan ta tabbatar da hakan ne a wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan Anipr, SP Josephine Adeh, ta fitar ta hannun kwamishinan ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja.
“Rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya Abuja na son tabbatar da wani hari ba gaira ba dalili da haramtacciyar kungiyar Musulunci ta Najeriya, wadda aka fi sani da ‘yan Shi’a, ta kai wa wasu jami’an rundunar ‘yan sandan Najeriya da ke ofishin babban birnin tarayya Abuja da ke Wuse Junction ta hanyar mota. An kashe jami’an ‘yan sanda biyu (2), uku sun sume a asibiti, sannan uku (3) motocin ‘yan sanda da ke sintiri sun kone kurmus.
“Haramtacciyar kungiyar ta kai hari a shingen binciken ’yan sanda ba tare da wani dalili ba, suna rike da adduna, da bama-bamai (bama-bamai na cikin gida a cikin kwalabe da kananzir), da kuma wukake.
“Yayin da aka kama da dama, kwamishinan ‘yan sandan babban birnin tarayya, CP Benneth C. Igweh, Psc. mni. Ya yi Allah-wadai da harin da aka kai kan jami’an ‘yan sanda. Ya yi alkawarin kawo wadanda ke da hannu a ciki.
KBC Hausa
Domin samun sauran shirye shiryenmu zaku iya biyo mu ta wannan shafukan👇
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj