Magoya Bayan Waiya Sun Fusata Kan Kin Naɗa Shi Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai a bikin Karɓar Gwamna a APC

IMG 130742 12226 1770898081134

Magoya bayan Kwamishinan Yaɗa Labarai na Jihar Kano, Ibrahim Abdullahi Waiya, na ci gaba da nuna bacin ransu kan yadda aka sanya shi memba kawai a Kwamitin Yaɗa Labaran Karɓar Gwamna Abba Kabir Yusuf zuwa APC, maimakon nada shi a matsayin Shugaban Kwamitin.

Rikicin ya fi fitowa fili ne a kafafen sada zumunta, musamman Facebook, inda magoya bayan Waiya ke wallafa sakonni da sharhi suna nuna rashin jin daɗinsu.

An dai naɗa tsohon Kwamishinan Yaɗa Labarai, Malam Muhammad Garba, a matsayin Shugaban Kwamitin, yayin da Sunusi Bature Dawakin Tofa, Daraktan Janar na Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a na Gidan Gwamnatin Kano, aka naɗa shi a matsayin Sakataren kwamitin.

Wannan mataki ya haifar da ce-ce-ku-ce a tsakanin magoya bayan jam’iyyar, inda wasu ke kallon lamarin a matsayin raini ga Waiya

Tuni dai magoya bayan Kwamishinan suka fara kiran shugabannin APC da su sake duba tsarin kwamitin domin kauce wa rikici da rarrabuwar kai a cikin jam’iyyar.

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *