Majalisar Wakilai ta gayyaci kantoman riko na Jihar Rivers

IMG 20250417 124743

Kwamitin wucin gadi da ke kula da lamarin Jihar Rivers ya gayyaci Kantoman riko na jihar, Vice Admiral Ibok-Ete Ibas (mai ritaya.), da ya bayyana a gabansu ranar Alhamis domin gudanar da zaman tattaunawa.

Wannan na cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Majalisar Wakilai, Akin Rotimi (Jnr), ya fitar a ranar Laraba.

Kwamitin da ke da mambobi 21, ƙarƙashin jagorancin shugaban masu rinjaye na Majalisar, Farfesa Julius Ihonvbere, an kaddamar da shi ne a ranar Talata daga Shugaban Majalisar, Abbas Tajudeen.

Majalisar Wakilai ce ta kafa kwamitin biyo bayan kudurin da Majalisar Tarayya ta amince da shi, wanda ke goyon bayan ayyana dokar ta-baci da Shugaban Ƙasa ya yi a Jihar Rivers.

A cewar Rotimi cikin sanarwar, an fitar da gayyatar ne a zaman farko da kwamitin ya gudanar a ranar Laraba, bayan kaddamarwar da Shugaban Majalisar ya yi a ranar Talata, 15 ga Afrilu, 2025.

Ya bayyana cewa zaman ya ba da damar tattauna rahotannin farko da abubuwan da ke faruwa tun bayan da kantoman ya hau mulki a Jihar Rivers.

Daily Nigerian

For more information about  Alfijir labarai/Alfijir news follow here  👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/KoLt2IMlnQfJPP6zNrcNKD

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *