Mutane 66 Suka Rasa Ransu Sakamakon Shan Wani Maganin Tari A Kasar Gambia

Alfijr ta rawaito wani gurbatattun magunguna hudu na da nasaba da raunin koda, a cewar Hukumar Lafiya ta Duniya.

Alfijr Labarai

Majalisar Binciken Likitoci ta Gambia ta kuma fitar da sanarwar.

Gambia ta kaddamar da wani binciken gaggawa zuwa gida-gida, bisa zargin wani maganin tari da maganin sanyi da ake kyautata zaton ya haddasa mutuwar yara sama da 60 sakamakon raunin koda a kasar da ke yammacin Afirka.

Daraktan Lafiya Dokta Mustapha Bittaye ya tabbatar wa Kamfanin Dillancin Labarai na Associated Press, cewar, yawan mace-macen yara kanana sakamakon mummunan rauni na koda, lamarin da ya jefa girgizar kasa a fadin kasar mai mutane miliyan 2.4 da ma duniya baki daya.

Alfijr Labarai

“WHO ta fitar da sanarwar gargadin magunguna guda hudu da aka gano a Gambiya wadanda ke da alaka da munanan raunukan koda da kuma mutuwar yara 66, kamar yadda Darakta-Janar na WHO Tedros Adhanom Ghebreyesus a cikin wata sanarwa da aka bayar Laraba. ”

Magungunan guda hudu sune tari da maganin sanyi da ake samarwa a Indiya, in ji sanarwar ta WHO.

Yayin da ya zuwa yanzu an gano gurbatattun kayayyakin a Gambiya, mai yiwuwa an rarraba su zuwa wasu kasashe, in ji shi.

Hukumar ta WHO tana bin diddigin bincike tare da kamfanin da hukumomin da ke da tsari a Indiya, in ji ta.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

Facebook. Best seller Channel
YouTube. Best Seller Channel
Twitter. @Musabestseller
Instagram. @musa_bestseller

Slide Up
x

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *