Najeriya na asarar biliyan 40 duk shekara saboda damfara a daukar ma’aikata — Ina Ji EFCC

FB IMG 1740836224096

Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa  ta EFCC, Ola Olukoyede, ya bayyana cewa Najeriya na rasa sama da Naira biliyan 40 duk shekara saboda damfara da ake yi ta daukar ma’aikata.

Olukoyede ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin wata ganawa da jami’an Kungiyar Tattaunawa da Ma’aikata ta Najeriya (NECA) a hedkwatar EFCC da ke Abuja.

Shugaban EFCC ya ce binciken da ya gudanar a shekarar 2007 kafin ya shiga hukumar, ya gano cewa ma’aikata  suna cutar juna ta hanyoyi daban-daban.

“A shekarar 2007, kafin na zo EFCC, na yi bincike kan damfara a daukar ma’aikata, inda na bincika yadda masu daukar aiki ke damfarar ma’aikata, da kuma yadda ma’aikata ke damfarar kamfanoni da hukumomi da suke aiki a cikinsu. Tun a wancan lokacin na gano cewa Najeriya na asarar sama da Naira biliyan 40 duk shekara saboda wannan matsala,” in ji Olukoyede.

Ya ce tun bayan hawansa shugabancin EFCC, hukumar ta ceci miliyoyin nairori bayan ta gano cewa akwai dimbin marasa aiki da ke karbar albashi daga gwamnatin tarayya.

Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news zaku iya bibiyarmu ta 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/IqPyC2oGzdQ9NudcMXFqHZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *