Najeriya Na Kan Tsini – In Ji Sarkin Musulmi Sa’ad Abubakar

FB IMG 1707995180137

Mai alfarma sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III ya bayyan fargabar cewa Najeriya na fuskantar barazanar tsaro bisa la’akari da yadda dumbin matasan kasar ke fama da rashin aikin yi da yunwa.

Alfijir labarai ta rawaito Sarkin Musulmin ya yi wadannan kalamai ne yayin da yake jawabi a wani taron majalisar sarakunan gargajiya ta arewacin Najeriya ranar Laraba a Kaduna.

Muhammad Sa’ad Abubaakr III ya ce ” mun shiga wani sabon zango na shugabanci. An samu sabbin gwamnoni inda kuma wasu suka yi tazarce a karo na biyu amma har yanzu muna fama da matsalar tsaro.

Babban matsalar ma ita ce karuwar talauci. Mafi yawancin mutanenmu ba su da hanyoyin samun abin da za su ci su sha”.

Ya kara da cewa idan dai har gwamnoni na son zaman lafiya a jihohinsu, dole ne su sama wa matasa aikin yi sannan dole ne su yi aiki tare da sarakunan gargajiya.

“Dole ne mu sama wa dimbin matasanmu masu zaman kashe wando ayyukan yi. Na sha fadar cewa muna wasa da bakin wuta. Saboda samun miliyoyin matasa ba tare da ayyukan yi ba sannan suna fama da yunwa, hakan na nufin muna fuskantar barazana.”

Daga karshe ya ce ya yi amannar cewa za a samu mafita duk da cewa “Najeriya ba ta taba gaza samar da mafita ba illa dai kawai ba a iya aiwatarwa”.

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H3iC9eVfJI012LJzvCQn5V

Slide Up
x

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *