Kimanin lauyoyi masu zaman kansu 500 ne suka yi alƙawarin kare, Nasir Yusuf Gawuna a kotun koli.
Alfijir labarai ta rawaito Joseph Onwudiwe, mai magana da yawun lauyoyin a karkashin kungiyar masu kula da dimokuradiyya da doka ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a Abuja a yau Talata.
Mista Onwudiwe ya ce an yi hakan ne domin inganta dimokuradiyyar kasar.
“Yan Najeriya sun lura sosai da halin da ake ciki a jihar Kano dangane da zaben gwamnan da aka yi a ranar 18 ga Maris.
“A matsayinmu na kungiyar da ke da alhakin kare mutuncinmu da dabi’unmu na dimokuradiyya, yanzu ba mu gamsu da hare-haren maganganu marasa dadi da ake kaiwa bangaren shari’a ba.
“Kuma wani yunƙuri na bata wa Kotun suna ba. Ba za mu sake naɗe hannayenmu a matsayin lauyoyi ba, mu kalli yadda ake ci gaba da cin zarafi da cin mutuncin sashen shari’a ba,” in ji shi.
Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/H47OrRBUPHYEeNqV0vwlQp
Gaskiya sun kyauta sosai wallahi.