Shigowar ka APC ba zai hana a EFCC da ICPC cigaba da bincikarka ba”. Inji Abdullahi Abbas

IMG 20250418 154314

Shugaban jam’iyyar APC a Kano, Abdullahi Abbas ya yi kira ga jagoran jam’iyyar NNPP na ƙasa, Rabi’u Musa Kwankwaso da kar ya shigo APC da kungiyar siyasarsa mai suna Kwankwasiyya.

Abbas ya bayyana haka ne a wani taron manema labarai da ya gabatar a sakatariyar APC ta Kano a yau Juma’a, ya kara da cewar ba ruwan APC da wata ƙungiya ta siyasa cikin jam’iyyar.

Duk da cewa Abbas bai fadi Kwankwasiyya ba, amma a jawabin nasa ya nuna cewa babu wata kungiya ko jam’iyyar siyasa da za a bari ta shigo cikin APC.

Ya kara da cewa duk masu tururuwar dawowa APC ba za a ki karbar su ba amma sai sun je mazabu su sun yi rijista.

Ya kuma ce dukkanin shugabannin da ke rike shugabancin jam’iyyar a matakai daban-daban a jihar suna nan akan mukaman su.

” Muna sanar da duk wanda yake son shigowa APC cewa kofar mu a bude take, amma ka sani shigowar ka APC ba zai hana a EFCC da ICPC cigaba da bincikarka ba”. Inji Abdullahi Abbas

Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news ku shiga nan  👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/KoLt2IMlnQfJPP6zNrcNKD

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *