Takaddama Ta Janyo Matar Ɗan Sanda Ta Banka Masa Wuta A yayin Wata

B9

Daga Aminu Bala Madobi

Wata mata mai suna Sarah Ayinde, ta bankawa mijinta wuta, Mai suna Abidemi Ayinde, jami’in ‘yan sandan jihar Ogun Dake zaune a unguwar Iperu da ke jihar Ogun.

Majiyar da ta nemi a sakaye sunan ta ta ce lamarin ya faru ne bayan da ma’auratan suka yi wata ‘yar takaddama.

Majiyar ta ce a ranar Lahadin da ta gabata ce 22 ga watan Disamba ne rigimar ta ta’azzara, inda matar ta kona dan sandan a wani yunkurin ramuwar gayya.

Majiyar ta ce, “Matar tasa ta kona wani karamin ofishin ‘yan sanda. Bayan wata takaddama da suka yi, sai matar ta banka masa wuta.

Yanzu haka mijin yana kwance a asibiti.” Da yake tabbatar da faruwar lamarin a wata tattaunawa da ya yi da manema labarai ta wayar tarho, mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar, Omolola Odutola, ya bayyana cewa wanda abin ya shafa na kwance a asibiti, kuma tuni aka cafke wadda ake zargin.

Domin samun sauran shirye-shiryen Alfijir labarai/Alfijir news zaku iya bibbiyarmu ta 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *