Ƙungiyar lauyoyi ta ƙasa ta buƙaci ƴan sanda su binciki Kwankwaso bisa kalaman da ya yi kan shari’ar zaben gwamna

FB IMG 1769257397994

Ƙungiyar Lauyoyin Nijeriya (NBA) ta ce ta yanke shawarar shigar da ƙorafi ga Rundunar ’yan sandan Nijeriya da sauran hukumomin tsaro domin a binciki ikirarin da ke nuna katsalandan a harkokin shari’a.

Hakan ya biyo bayan kalaman da aka jingina wa Rabiu Musa Kwankwaso, jagoran jam’iyyar NNPP, inda ya ce a lokacin rikicin zaɓen gwamnan Kano na 2019 ya kai Abba Yusuf wurin alkalan Kotun Ƙoli bayan INEC ta ayyana zaɓen a matsayin wanda bai kammala ba.

NBA ta ce irin waɗannan ikirari na iya raunana amincewar jama’a ga ’yancin kai na bangaren shari’a da tsarin adalcin zaɓe.

Ƙungiyar ta jaddada cewa shigar da ƙorafi ba yana nufin an riga an ɗauka akwai laifi ba, sai dai domin a gudanar da cikakken bincike mai zaman kansa.

NBA ta kuma sake tabbatar da jajircewarta wajen kare bin doka da oda, da ’yancin kai da mutuncin kotunan Nijeriya.

Daily Nigerian

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *