Kungiyar Samarin Tijjaniyya Ta Kasa Tayi Allah Wadai Da Tashin Gwauron Zabi Da Man Fetur Yayi A Fadin Kasar

Tijjaniyya

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Kungiyar ta fitar sakamakon sanarwar data fito na Kara farashin mai da kamfanin Samar da man fetur na Kasa yayi.

Sanarwar da Sakataren Kungiyar Samarin Tijjaniyya ta Kasa Shehu Tasiu Ishaq da sakataren yada labarai na Kungiyar Abubakar Balarabe Kofar Naisa suka sanyawa hannu tace bisa la’akari da halin da “Yan kasa ke ciki akwai bukatar a duba lamarin.

Kungiyar ta bukaci Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya rage farashin Man fetur din a maimakon Kara farashin sa, domin saukakawa al’umar Najeriya.

Sanarwar daga nan sai ta bukaci al’umar Najeriya su cigaba dayin addu’oi na neman samun sassaucin al’amura da samun cikakken tsaro da wadatar arziki a Kasa baki daya.

Domin samun sauran shirye shiryenmu zaku iya biyo mu ta wannan shafukan👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *