Ana Wata! Likitoci A Kano Sun Bayyana Ranar Tafiya Yajin Aiki Tare Da Dalilinsu

FB IMG 1717836629517

Likitoci a Jihar Kano, sun bayyana damuwarsu kan rashin isassun likitocin da za su ke duba marasa lafiya, wanda hakan ya sa suke shirin tafiya yajin aiki daga ranar 1 ga watan Oktoba.

Alfijir labarai ta rawaito ʙungiyar lkitocin Asibitocin Gwamnati da Likitocin Haʙora ta ʘasa ce, ta bayyana hakan, yayin wani taron manema labarai da sakataren ʙungiyar, Dokta Anas Idris Hassan, ya jagoranta.

Ya ce gwamnatin jihar ta amince a watan Yuni za ta biya musu buʙatunsu, amma har yanzu ba ta ɗauki wani mataki ba.

Ɗaya daga cikin muhimman batutuwan da suke korafi a kai shi ne rashin biyansu alawus bayan wucewar annobar COVID-19, wanda Gwamnatin Tarayya ta biya tun a 2021, amma Gwamnatin Jihar Kano har yanzu ba ta biya ba.

Dokta Anas ya kuma bayyana cewa likitocin da aka ɗauka aiki a watan Satumban 2023 ba su samu albashinsu ba.

Likitocin sun kuma koka kan yanayin asibitocin Kano da rashin manyan kayan aiki. Babbar matsalar ita ce ʙarancin likitocin da za su ke duba marasa lafiya.

A Kano, akwai kimanin mutum miliyan 20, amma likitoci 600 ne kawai suke duba su, wanda hakan ke nufin likita ɗaya na kula da marasa lafiya 33,000.

Wannan adadi ya saɓa da ʙa’idar da Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta tsara.

Saboda waɗannan matsaloli, likitocin suka yanke shawarar tafiya yajin aiki daga ranar 1 ga watan Oktoba.

Domin samun sauran shirye shiryenmu zaku iya biyo mu ta wannan shafukanšŸ‘‡

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai šŸ‘‡šŸ‘‡

https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *