An Kama Wata Mahaifiya Bisa Zargin Garkuwa Da ‘Yarta Ta Cikinta

ALFIJIR 4

Ana tuhumar mahaifiyar yarinyar nan mai shekara shida da ta ɓata a Afirka ta Kudu da laifi fatauci da garkuwa da diyarta.

Alfijir labarai ta rawaito an gabatar da wannan tuhuma ne a kan Kelly Smith tare da saurayinta da wasu mutane biyu a shari’ar da ta ba da mamaki a kasar.

Joslin Smith ta ɓata a wajen gidansu da ke kusa da birnin Cape Town a ranar 19 ga watan Fabarairu.

Bincike ya gano rigarta da jini a jiki, amma ba a ga yarinyar ba, duk da binciken da aka ƙaddamar na hadin-gwiwa da sojojin sama da jirage marasa matuka da karnuka.

Kafin wannan lokaci mahaifiyar yarinya ta ce ba za ta saduda ba har sai an gano diyarta ta a raye.

A cikin kowanne sa’a biyar ana samun rahotannin ɓatan yara a Afirka ta Kudu.

BBC

Domin Samun sauran shirye shiryenmu, Zaku iya bibiyarmu a

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijir Labarai 👇

https://chat.whatsapp.com/CJ2q8cmhhOxFY6OEgwV5vk

Slide Up
x

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *