Cigaba: BUK ta ƙaddamar da Sabuwar Manhajar Duba Sakamako Jarabawa

FB IMG 1743499475945

Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta kaddamar da wani tsari na yanar gizo wanda zai baiwa dalibai damar shiga da duba sakamakon kammala karatunsu ta hanyar lambobi.

Wannan sabon yunkuri shine karo na farko da cibiyar ta samar da sakamako ta hanyar irin wannan dandali.

An sanar da shirin ne a cikin wata takarda mai dauke da sa hannun mataimakin magatakarda kuma shugaban hukumar kula da harkokin jama’a Lamara Garba Azare.

A cewar sanarwar jami’ar, tsarin da myBUK Team ya kirkira kuma yana bawa ɗalibai damar dawo da sakamako kai tsaye ta hanyar amfani da sashen rajistar dalibai.

Takardun sakamakon za su nuna a sarari na kowane kwasa amma dole ne ɗaliban da suka kammala shekarar ƙarshe su jira amincewar Majalisar Dattawa kafin su sami sakamakonsu.

Daya daga cikin shugabannin kungiyar dalibai a Jami’ar, Bilal Muhammad Bello, ya yabawa ci gaban da aka dade ana jira tare da bada tabbacin cewa wannan zai rage damuwar dalibai da kuma kawar da jinkiri da aka samu wajen samun sakamakon.”

“Wannan tsarin yana ba ɗalibai damar sanya ido kan ci gaban karatun su tare da kawar da cunkoson da ake samu na jama’a a a allon manna sakamakon jarabawa.”

Da yake tsokaci kan zaman sa a matsayin Sanata na 24 na SUG mai wakiltar Sashen Sadarwa, Bello ya ce. “Na ba da shawarar samun damar samun sakamako ta yanar gizo a lokacin da nake majalisar dalibai, Alhamdulillah, wannan hangen nesa ya zama gaskiya.”

RN

For more information about  Alfijir labarai/Alfijir news follow here  👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/KoLt2IMlnQfJPP6zNrcNKD

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *