Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da sauke Alhaji Shehu Wada Sagagi daga mukaminsa na Kwamishinan Ma’aikatar Zuba Jari, Kasuwanci da Masana’antu da nan take.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya sanya wa hannu.
Wannan mataki ya fara aiki nan take.
Gwamnan ya umarci Alhaji Sagagi da ya mika ragamar ma’aikatar ga Babban Sakataren ma’aikatar.
Ana sa ran zai kammala mika ragamar aiki zuwa gobe da safe.
Hakazalika Gwamna Yusuf ya gode masa bisa gudunmawar da ya bayar a lokacin da yake rike da mukamin.
Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835
Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇
https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t