Hukumar tsaron farin kaya ta DSS ta bada belin shugaban kungiyar kwadago na Najeriya, NLC, Joe Ajaero bayan Kama shi da tayi a safiyar litinin.
Alfijir Labarai ta rawaito wani mai rajin kawo cigaban jama’a kuma tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AAC, Omoyele Sowore ne ya bayyana hakan a wani sako da ya wallafa a shafin sa na X a daren Litinin.
An kama Ajaero a safiyar ranar Litinin a filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe dake Abuja, a akan hanyar sa ta zuwa kasar Ingila domin gudanar da wani aiki a hukumance.
Ajaero dai zai halarci taron kungiyar ‘yan kwadago da za a yi a Landan, wanda za a fara a litinin dinnan.
Domin samun sauran shirye shiryenmu zaku iya biyo mu ta wannan shafukan👇
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Ko a latsa nan don shiga Group Whatsapp na Alfijr Labarai 👇👇
https://chat.whatsapp.com/ELQRQyq1zGn7zpAVP8DwNj