Farfesa Usman Yusuf ya kai karar Kwankwaso gaban DSS kan zargin yi masa kalaman barazana da tunzura jama’a

IMG 194502 22526 1779475515023

A cikin takardar ƙorafin mai ɗauke da kwanan watan 22 ga Mayu, 2026, Farfesa Usman Yusuf ya ce kalaman sun biyo bayan sharhin da ya yi kan haɗakar siyasa da kuma batutuwan siyasar yankuna.

Ya bayyana cewa ko da yake Sanata Kwankwaso bai ambaci sunansa kai tsaye ba, amma bayanin da ya yi ya isa ya sa masu sauraro gane wanda ake nufi.

Farfesa Yusuf ya kuma yi zargin cewa Sanatan ya bukaci magoya bayan Kwankwasiyya da wasu ƙungiyoyin matasa su “tarwatsa” wanda ake magana a kansa da kalmar Hausa ta “fata-fata,” lamarin da ya ce na iya jawo tsoratarwa ko tashin hankali.

Premier Radio

Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835

Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *