Gwamnatin Kano ta shirya canzawa kasuwar Kayan marmari ta yan lemo mazauni zuwa Dan Goro
Kwamishinan Ƙasa da Safiyo na Jihar Kano, Alhaji Abduljabbar Umar Garko, ya bayyana matsayar gwamnati jim kaɗan bayan kammala zaman majalisar zartarwa na karo na 31 a gidan gwamnati.
Da yake jawabi ga manema labarai kan lamarin, kwamishinan ya ce zaman majalisar ya tattauna muhimman al’amura da suka shafi ci gaban jihar, musamman a fannoni daban-daban na raya ƙasa da walwalar al’umma.
Garko ya jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da ɗaukar matakai masu tasiri domin tabbatar da ingantaccen gudanar da mulki da kuma kawo sauƙi ga rayuwar jama’ar Kano.
Rahoton ya nuna cewa, wannan shi ne zama na 31 da majalisar ta gudanar tun bayan hawar gwamnatin yanzu, kuma an samu damar yanke shawarwari da dama da za su amfani jihar baki ɗaya.
Ga masu son bada talla ko shawarwari a kira wannan lambar +2348032077835
Domin samun sauran shirye-shirye Alfijir labarai/Alfijir news ku biyo mu ta nan 👇
https://twitter.com/Musabestseller?s=09
https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165
https://www.threads.net/@alfijirlabarai
https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12
https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag
Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇
https://chat.whatsapp.com/H5oBRaZBdCVIyOTIV5eMfb?mode=ac_t