Gwamnatin Najeriya Ta Amince Da Tallafin Naira Biliyan 4 Don Taimakawa Gidajen Mabuƙata

IMG 20250123 162712

Gwamnatin Tarayya ta amince da bayar da tallafin kuɗi na naira biliyan 4 domin taimaka wa gidaje masu rauni a cikin al’umma. Haka kuma, an ware naira biliyan 2 a matsayin bashi mara ruwa ga manoma, musamman waɗanda ke yankunan karkara, domin bunƙasa noma da cimma wadatar abinci. 

Ministan Harkokin Jin Kai da Rage Talauci, Farfesa Nentawe Yilwada, ya bayyana wannan tsari a wajen ƙaddamar da 2025 Nigeria Humanitarian Needs and Response Plan da aka gudanar a ofishin Majalisar Ɗinkin Duniya da ke Abuja ranar Alhamis. 

Tsarin tallafin zai tallafa wa gidaje akalla miliyan 10 da aka raba da muhallansu, tare da mayar da hankali ga mafi raunin cikin al’umma. 

Shirin bayar da tallafin kuɗi zai fara ne daga watan Fabrairu zuwa Afrilu, domin magance matsalolin gaggawa da ke fuskantar iyalai da rikici ya shafa, musamman a Arewa maso Gabas. 

For more information about  Alfijir labarai/Alfijir news follow here  👇

https://twitter.com/Musabestseller?s=09

https://www.facebook.com/profile.php?id=100089640289165

https://www.threads.net/@alfijirlabarai

https://www.youtube.com/@BestsellerChannel12

https://www.instagram.com/musa_bestseller?utm_source=qr&r=nametag

Alfijir labarai Alfijir News Whatsapp Group 👇👇

https://chat.whatsapp.com/IqPyC2oGzdQ9NudcMXFqHZ

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *